Ayzan Multimedia

Ayzan Multimedia

Share

Photos from Ayzan Multimedia's post 16/02/2026

Hadin gwiwar jami’an tsaro sun lalata manyan sansanonin ’yan bindiga uku a Jihar Kogi tare da kubutar da wasu mutanen da aka yi garkuwa da su a wuraren.

Arewa Updates ta rawaito cewa, wannan na cikin sanarwar da Kwamishinan Yada Labara na Jihar Kogi, Kingsley Femi Fanwo, ya fitar a ranar Lahadi 15 ga Fabrairu 2026.

Sanarwar ta ce hadin gwiwar ofishin Mai ba Shugaban kasa shawara kan Tsaro, rundunar Sojin ƙasar nan ta 12, rundunar ruwa, rundunar sama, ’yan sanda, jami’an DSS da kuma kungiyoyin sa kai da mafarauta ne s**a kai farmakin.

Sanarwar ta kara da cewa an lalata sansanonin gaba daya tare da kubutar da mutanen da aka tsare a wuraren, yayin da wasu da ake zargi s**a rasa rayukansu a yayin artabun.

Kazalika, Gwamnatin Jihar Kogi ta kai wadanda aka kubutar cibiyoyin lafiya domin kula da su, sannan daga baya za a mayar da su ga iyalansu.

Sanarwar ta bayyana cewa gwamnatin jihar na ci gaba da aiki da hukumomin tsaro domin dakile ayyukan ’yan bindiga a fadin jihar.

- Arewa Updates

Photos from Ayzan Multimedia's post 16/02/2026

Gobarar dai ta ɓarke ne daga ranar Asabar inda ta ci har zuwa Lahadi a wasu rukunin shaguna da ake yi wa laƙabi da Gidan Gilas, inda aka yi asarar kayayyaki na miliyoyin naira.

Hotuna da bidiyo da aka yaɗa sun nuna yadda hayaƙi s**a turnuƙe saman kasuwar, yayin da shaguna s**a k**a da wuta tare da ƙonewar kayayyakin masarufi masu ɗumbin yawa.

Want your university to be the top-listed University in Kano?
Click here to claim your Sponsored Listing.

Telephone

Address


Kano