Jaridar Hausa Reporters

Jaridar Hausa Reporters

Share

17/02/2026

RAHOTO:

Comrade Yakub Nasir Khalid ya bayyana cewa, Alhassan Doguwa shi ne ɗan siyasar da har yanzu ba shi da kima ko mutunci a gurin ’yan uwansa ’yan siyasa. Ya ƙara da cewa dun daga lokacin da ya bar mulki, babu wanda zai ƙara jin motsinsa, domin a cewarsa mutane suna tunawa ne da abin alheri ko kuma yadda aka mu’amalanci su.

Hakazalika, Comrade Khalid ya zargi cewa za a tuna da shi ne da abubuwan da ba su dace ba, ciki har da ta’addanci, cin zarafin mutane, da kuma cutar da matasan yankin Tudun Wada da Doguwa ta hanyar hana su damar yin karatu da amfani da jahilcinsu wajen rusa rayuwarsu baki ɗaya.

A ƙarshe, ya bayyana cewa suna barin al’amuransu a hannun Allah, tare da addu’ar Allah Ya isa game da damar yankin da aka lalata.

17 February, 2026

08/07/2025

Faɗa akayi ko kuɗin break ne ba'a basu ba?

Wa'inda s**ayi Islamiyya ne kaɗai zasu iya chanka 🤣

Photos from Jaridar Hausa Reporters's post 08/07/2025

Da Ɗumi-Ɗumi: Fiye da Ƴan Sa-kai 70 Sun Rasa Rayukansu a Fada da Ƴan B|ndiga a Kanam, Jihar Filato.

Aƙalla ƴan sa-kai 70 ne aka tabbatar da mutuwarsu a wani mummunan h4ri da ƴan b|ndiga s**a kai a yankunan Kukawa da Bunyun da ke ƙaramar hukumar Kanam, a jihar Filato. Wannan h4rin da ya girgiza al’umma ya faru ne da misalin ƙarfe biyu na ranar Litinin 7 ga watan yuli 2025, Inda aka ce ƴan sa-kai daga ƙaramar hukumar Wase suna kan hanyarsu ta kai farmaki kan mafakar ƴan b|ndiga kafin su faɗa cikin kwanton-baunar ƴan b|ndigan.

Aliyu Baffa, Shugaban rundunar ƴan sa-kai na Kukawa, ya bayyana cewa:

> “Fiye da ƴan sa-kai 70 ne aka ka$he a wannan h4ri. Har yanzu ana ci gaba da neman wasu gawarwakin a dazuka da gonaki. Bazamu taɓa iya mantawa da wannan abun ba.”

A cewarsa, Lamarin ya faru ne kimanin kilomita ɗaya daga garin Kukawa, A hanyarsu ta zuwa wata mafakar ƴan bindiga da ke cikin dajin gwamnati da ake kira Madam Forest, Wanda ke iyaka da jihohin Bauchi da Taraba. Wannan daji dai an daɗe ana kallonsa a matsayin mafaka ta manyan ƙungiyoyin ƴan ta’4dda.

Baffa ya ƙara da cewa bayan fadan, An gano gawarwakin wasu daga cikin ƴan sa-kai a gonaki daban-daban.

> “Mun binne fiye da mutum 60 a Kukawa kawai. Muna da tabbacin cewa har yanzu akwai gawarwaki a cikin daji. Wasu daga cikin ƴan b|ndigar da s**a tsira sun bayyana cewar sun ci galabar wannan yaƙ|n, Lamarin da ya ƙara nuna girman harin,” in ji shi.

A wani ɓangare na rahoton, Musa Ibrahim, Mazaunin ƙauyen Bunyun da ke cikin gundumar Nyalun, ƙaramar hukumar Wase, Ya bayyana cewa ƴan b|ndigar sun kai h4ri kan ƙauyensu inda s**a ka$he ƴan sa-kai goma da ke kan bakin aiki a yankin.

> “Sun ƙ0ne gidaje da dama, Sun kuma tayar da hankalin al’umma. Mutane da yawa sun tsere zuwa dazuka domin tsira da rayukansu,” in ji Musa cikin damuwa.

Rahotanni daga yankin na nuna cewa jama’a na cikin firgici da fargaba, Yayin da ake ci gaba da bin sahun ƴan b|ndigar da s**a tsere daga wajen harin.

Hukumomi dai na ci gaba da bincike da ƙoƙarin dawo da zaman lafiya a yankin, Sai dai al’umma na kira da a kawo ɗauki cikin gaggawa domin daƙile irin wannan rikicin mai nasaba da rashin tsaro.

Allah ya kyauta! 🤲🏻

— Faisal Sadauki

Want your business to be the top-listed Media Company in Kano?
Click here to claim your Sponsored Listing.

Telephone

Website

Address


Kano