Kokiya
09/06/2026
Ɗan takarar sanatan Kano ta Tsakiya a jam'iyyar NDC, Dr. Nasiru Yusuf Gawuna, ya ci gaba da gudanar da tattaunawa mai zurfi domin komawa jam’iyyar ADC, tare da neman tikitin takarar gwamna na jam’iyyar a zaɓen shekarar 2027.
Rahotanni daga jaridar Punch, sun nuna cewa tattaunawar sauya sheƙar na ci gaba da samun tagomashi, yayin da ake sa ran Gawuna zai shiga ADC domin fafatawa a zaɓen gwamnan Kano mai zuwa.
Wacce shawara za ku baiwa Gawuna?
08/06/2026
DA ƊUMI ƊUMI: Tsohuwar ministar jinkai Sadiya Farouq ta nemi kotu ta soke sammacin k**a ta
Tsohuwar ministar harkokin jin-ƙai, Sadiya Farouq, ta roƙi babbar kotun Abuja da ta soke sammacin k**a ta da aka bayar a kanta kan zargin da ake yi mata tare da wasu tsofaffin jami’an ma’aikatar.
Farouq ba ta halarci zaman kotun ranar Litinin ba, inda lauyanta ya bayyana cewa tana fama da matsalar lafiya. Sai dai lauyan EFCC ya ƙi amincewa da sauraron buƙatar, yana mai cewa ba za a iya yin hakan ba kafin a gurfanar da ita a hukumance.
Lauyan Farouq ya dage cewa buƙatar tasa ta dace a saurare ta, domin tana neman a soke sammacin k**a da kotu ta bayar a ranar 16 ga Afrilu.
Bayan sauraron ɓangarorin biyu, Mai Shari’a Jude Onwuegbuzie ya ɗage shari’ar zuwa ranar 10 ga Yuni domin yanke hukunci kan buƙatar da Farouq ta gabatar.
Click here to claim your Sponsored Listing.
Category
Website
Address
Kano