N R HAUSA TV

N R HAUSA TV

Share

28/06/2025

Mai dakin shugaban kasa Mr. Remi Bola Ahmad Tinubu ta bada tallafin Naira miliyan 110 ga iyalan yan wasan jihar Kano 22 wadanda s**a rasu sakamakon hatsarin a hanyarsu ta dawowa gida bayan kammala gasar wasannin motsa jiki ta kasa.

Da take gabatar da tallafin ga iyalan mamatan, Mai dakin shugaban kasa Mrs. Remi Tinubu wadda ta samu wakilcin Mai dakin mataimakin shugaban majalisar dattijai Hajiya Laila Barau Jibril, ta bayyana alhininsa bisa rasuwar su.

28/06/2025

‎Ana neman tono gawar tsohon Gwamnan Jihar Oyo, Otunba Christopher Adebayo Alao-Akala, domin yin gwajin jini (DNA) da nufin tantance halastattun ’ya’yansa da za su ci gadon dukiyar da ya bari.

Me zaku ce?

28/06/2025

An shiga ruɗani bayan sace wata mashahuriyar Tukunya da ta kai kimanin shekaru 30 ana girki da ita.

Matashi Abdurrahim Umar Kura shi ne ya wallafa ɓacewar Tukunyar wanda ya ce sun girgiza da jin sace wannan Tukunya la'akari da yadda ɗanɗanan girkin ta daban yake da sauran Tukwane.

Zalika matasin ya bukaci duk wanda yaga wannan Tukunya tasu da ya taimaka ya tuntube su.

Want your business to be the top-listed Media Company in Kano?
Click here to claim your Sponsored Listing.

Address


Kano