SHUNI

SHUNI

Share

09/06/2026

Sanata Ali Ndume ya bayyana cewa fushin da ‘yan Najeriya ke yi kan matsin rayuwa da wahalhalun tattalin arziki na ƙaruwa, inda ya gargadi jam’iyyar APC da Shugaba Bola Tinubu cewa ba za su raina ƙarfin hamayya ba yayin shirin zaɓen 2027.

A lokaci guda, Ndume ya roki gwamnatin Amurka da ta kafa sansanin soja a Dutsen Mandara na Jihar Borno domin murkushe ragowar mayakan Boko Haram, yana mai jaddada bukatar haɗin kai tsakanin ƙasashen duniya da Najeriya wajen yaki da ta’addanci.

Sanata Ndume ya yi wannan bayani ne a daidai lokacin da ake tunkarar babban zaɓen 2027, inda ya nuna damuwarsa kan yadda rikicin tattalin arziki da tsaro ke shafar al’umma.

09/06/2026

GWAMNA FINTIRI YA NAƊA DR. SUMAYYA SABO A MATSAYIN JAGORAR ADAMAWA DIGITAL ACADEMY

Gwamnan Jihar Adamawa, Rt. Hon. Ahmadu Umaru Fintiri, CON, ya amince da naɗin Dr. Sumayya Babangida Sabo a matsayin Programme Coordinator na Adamawa Digital Academy, a wani mataki na ƙara ƙarfafa shirin sauya fasalin jihar ta hanyar ilimin zamani da fasahar dijital.

A cewar sanarwar da Babban Sakataren Yaɗa Labaran Gwamna, Humwashi Wonosikou, ya fitar a ranar 9 ga Yuni, 2026, Dr. Sabo ƙwararriya ce a fannin Information Systems, gudanar da ilimi, shirye-shiryen ƙere-ƙere, da kula da harkokin fasahar sadarwa. A halin yanzu tana aiki a matsayin Tutor da IT Coordinator a American University of Nigeria, AUN, da ke Yola.

Sabon aikin nata zai haɗa da kula da shirye-shiryen Academy ɗin, karɓar sabbin ɗalibai, hulɗa da masu ruwa da tsaki, gudanar da harkokin ilimi, da aiwatar da haɗin gwiwar dabaru. Gwamnatin Adamawa ta ce shirin na daga cikin Adamawa 2.0 Digital Transformation Agenda, wanda ke da burin horar da matasa da ma’aikatan gwamnati sama da 100,000 kan fasahohin dijital da sabbin dabarun zamani.

Want your business to be the top-listed Media Company in Jimeta?
Click here to claim your Sponsored Listing.

Telephone

Address


Jimeta
640101