AMT News
24/06/2026
Jam’iyyar PDP ta bai wa Farfesa Isa Ali Pantami takardar shaidar zama ɗan takarar gwamnan Gombe
Jam’iyyar PDP ta ƙasa ta bai wa Professor Isa Ali Pantami takardar shaidar zama halastaccen ɗan takararta na gwamnan jihar Gombe a zaɓen shekarar 2027.
Wannan na ƙunshe ne a cikin wani saƙo da Abba Sani Pantami, ya wallafa a shafinsa na Facebook, inda ya ce an miƙa takardar shaidar ne yayin wani taron jam’iyyar da aka gudanar a Abuja.
A cewar saƙon, PDP ta gudanar da taron Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NEC) tare da rantsar da sabbin shugabanninta na wa’adin 2026 zuwa 2030.
Saƙon ya ƙara da cewa jam’iyyar ta kuma bai wa sauran ‘yan takararta na gwamna takardun shaidar zama halastattun ‘yan takara bayan an sanya sunayensu cikin jerin ‘yan takarar da aka ce za su wakilci jam’iyyar a zaɓen 2027.
Yayin da Pantami ke zayyano wasu tarin nasarori da PDP tayi a Gombe
Yayin da magoya baya ke taya Pantami murnar samun takarar gwamna a jam'iyar PDP a Gombe
Facebook BBC Hausa RFI Hausa
Click here to claim your Sponsored Listing.
Category
Contact the business
Telephone
Website
Address
Gombe