Bitkova Digital Hub
13/03/2026
Ramadan Reminder | Day 24
Manzon Allah ﷺ ya ce: Allah Ya ƙasƙantar da mutumin da Ramadan ya zo masa, sannan watan ya wuce bai samu gafarar Allah ba.
(Sunan al-Tirmidhi 3545)
Ma’anar Hadisin:
Ramadan wata ne na rahama da gafara. Allah yana ba bayinsa dama su tuba, su ƙara ibada, su nemi gafara. Idan mutum ya samu wannan wata amma bai yi anfani da shi ba, wannan babban hasara ne gare shi.
Darussa daga hadisin:
1️⃣ Ramadan babbar dama ce ta neman gafarar Allah.
2️⃣ Kada mu yi sakaci da ibada, sallah, Qur’ani, azumi da addu’a a watan Ramadan
3️⃣ Lokaci yana wucewa da sauri, don haka a yi anfani da Ramadan kafin ya ƙare.
4️⃣ Babbar hasara ne mutum ya rasa gafara a wannan wata mai albarka.
Allah Ya sa mu dace da samun gafararSa a Ramadan.
Kada ku manta muna cigaba da registration na Ajin Cryptocurrency 2026A
🌍https://bitkova.com/our-hub
12/03/2026
Ramadan Reminder | Day 23
An karɓo daga Ibn Abbas (RA) ya ce:
Manzon Allah ﷺ shi ne mafi kyauta a cikin mutane. Kuma yakan fi yawan kyauta a watan Ramadan, lokacin da Mala’ika Jibrilu yake zuwa wajensa. Jibrilu yana zuwa wajensa kowace dare a Ramadan, suna karanta Al-Qur’ani tare. Saboda haka Manzon Allah ﷺ ya fi iska mai gudu wajen yawaita alheri da kyauta.
Sahih Bukhari hadith mai lamba ta 3554
Ma’anar Hadisin:
Hadisin yana nuna cewa kusanci da Al-Qur’ani da yawaita ibada yana ƙara wa mutum son yin alheri da taimakon mutane. Shi ya sa Manzon Allah ﷺ yake ƙara karamci sosai a Ramadan.
Darussa daga Hadisin:
Ramadan lokaci ne na ƙara sadaka da taimako ga mutane.
Karatun Al-Qur’ani yana gyara zuciya kuma yana ƙara son alheri.
Ya kamata mu koyi karamci da halin Manzon Allah ﷺ musamman a wannan wata.
Allah ya sa mu zama masu yawan alheri a Ramadan. 🤲
Kada ku manta muna cigaba da registration na Ajin Cryptocurrency 2026A
🌍https://bitkova.com/our-hub
10/03/2026
Ramadan Reminder | Day 21
Daga A’isha (Allah Ya yarda da ita) ta ce:
“Manzon Allah ﷺ ya kasance idan ya shiga kwanaki goma na ƙarshe na Ramadan, yana ƙara ƙaimi wajen ibada, yana tsarkake kansa, yana tashi da dare yana yin ibada, kuma yana tashe iyalinsa su yi ibada tare da shi.”
Bukhari ne ya ruwaito shi
Bukhari 2024.
Ma’ana a taƙaice:
Lokacin kwanaki goma na ƙarshe na Ramadan, Manzon Allah ﷺ yana ƙoƙari sosai wajen tsarkake zuciya da jiki, yana tashi dare yana salla da addu’a, kuma yana ƙarfafa iyalinsa su yi haka tare da shi. Wannan yana nuna mana muhimmancin ƙoƙari da himma a cikin kwanaki goma na ƙarshe.
Kada ku manta muna cigaba da registration na Ajin Cryptocurrency 2026A
🌎 https://bitkova.com/our-hub
09/03/2026
Ramadan Reminder| Day 20
Daga A’isha (Allah Ya yarda da ita) ta ruwaito cewa Manzon Allah ﷺ ya ce: “Ku nemi Lailatul Qadri a dararen witiri (21, 23, 25, 27, 29) na kwanaki goma na ƙarshe na watan Ramadan.”
Bukhari ne ya ruwaito shi.
Bukhari 2017
Ma’ana a taƙaice:
Manzon Allah ﷺ yana umartar mu da mu yi ƙoƙari sosai wajen neman Lailatul Qadri, musamman a dararen witiri daga cikin kwanaki goma na ƙarshe na Ramadan, domin a can ne mafi yawan yiwuwar samun ta.
Allah Ya ba mu dacewa da cin ribar wannan dare mai albarka.
Kada ku manta muna cigaba da registration na Ajin Cryptocurrency 2026A
🌎https://bitkova.com/our-hub
Click here to claim your Sponsored Listing.
Category
Contact the school
Telephone
Website
Address
Gombe