Sahara Reporters Hausa
01/04/2026
Labari da Dumi-Dumi
Hukumar INEC ta sanar da cewa za ta dakatar da mu’amala da dukkan bangarorin da ke takaddama akan shugabanci jam’iyyar ADC gaba daya, (Bangaren Sen. David Mark da bangaren Hon. Nafiu Bala).
Haka kuma, ba za ta sake sa ido ko halartar tarukan jam’iyyar ba, har sai kotu ta yanke hukunci na karshe.
Bugu da kari, INEC za ta cire sunayen su Sen. David Mark a matsayin shugabannin jam’iyyar na yanzu daga shafinta na yanar gizo (portal), domin tabbatar da bin umarnin kotu da kuma daukan matsayi na tsaka-tsaki.
12/03/2026
Yanzu ne lokaci mafi daɗi ka zama gwamna a Najeriya domin Tinubu na basu Bilyoyi kuɗi don rabawa — Akpabio ya yabawa Tinubu
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya ce a halin yanzu gwamnoni a Najeriya suna cikin wani lokaci mai matuƙar anfani idan aka kwatanta da shekarun baya.
Akpabio ya bayyana cewa a zamanin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, kuɗin da jihohi ke rabawa daga gwamnatin tarayya ya ƙaru sosai.
A cewarsa, a yanzu gwamnoni na rabon kusan Naira tiriliyan 1.9 zuwa tiriliyan 2.7, wanda ya fi abin da ake samu a gwamnatocin baya nesa ba kusa ba.
Ya ce da a ce shi ma gwamna ne a wannan lokaci, da ya fi jin daɗin mulki saboda yadda kudaden shiga na jihohi s**a ƙaru sak**akon sauye-sauyen tattalin arziki da gwamnatin Tinubu ta yi.
Akpabio ya ƙara da cewa yawancin gwamnoni ma na cewa abin da suke karɓa yanzu ya kai kusan sau huɗu na abin da ake samu a baya.
Tambaya yanzu ita ce: Shin karin kuɗin da jihohi ke samu zai haifar da sauƙin rayuwa ga talakawa kuwa?
11/03/2026
Babu maganar sulhu tsakanin mu da Amurka da Isra'ila, Inji Kwamandan sojin Iran, k**ar yadda jaridar Iran Times ta Rawaito.
Click here to claim your Sponsored Listing.
Category
Website
Address
Abuja