Arewa post 247
sakon Triple R.-na rarara
05/07/2026
Ya Yi Wa Tagwaye Ciki Duk Da Yana Soyayya da Mahaifiyarsu
Wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta ya yi zargin cewa wasu tagwaye mata masu suna Philomena da Patricia sun samu ciki daga mutum ɗaya mai suna Austin Angwe, wanda kuma ake cewa yana hulɗar soyayya da mahaifiyarsu, Alice Ukange, bayan rasuwar mijinta sakamakon harin 'yan bindiga.
A cewar rahoton, Angwe ya haɗu da mahaifiyar ne a shekarar 2017, inda s**a fara kasuwancin saye da safarar doya zuwa Lagos da Port Harcourt. An kuma yi zargin cewa yana hulɗa da kowacce daga cikin tagwayen a lokacin da suke karatu a Akwanga da Lafia.
Rahoton ya ce tagwayen sun haifi 'ya'yan Angwe a shekarar 2021, yayin da shi kuma ya yi iƙirarin cewa su ne s**a nemi ya yi hulɗa da su. Sai dai babu wata hujja mai zaman kanta da ke tabbatar da sahihancin waɗannan zarge-zargen.
05/07/2026
Tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Baba Tela, ya rasa 'ya'yansa biyu, Mustapha da Ummi, sakamakon wani mummunan hatsarin mota da ya rutsa da su a kan hanyar Bauchi zuwa Azare.
OMOLOGO.-'yan triple R na rarara
Triple R,kungiyar rarara na jagaba.
04/07/2026
Na Rasa Dalili" – Maisana'a Ya Yi Kuka Kan Yadda Mambobi Ke Barin Triple R, Ya Kare Rarara Da Cewa Shi Ne Ya Fi Kowa Amfanar Da Ƴan Fim.
04/07/2026
"Sun Harbe Shi A Ƙofar Gidansa" — Hawaye Sun Mamaye Jana'izar Hakimin Ƙauyen Kulodo, Ɗansa da Wasu Mutum Huɗu Bayan Harin Ƴan Bindiga 150 a Sokoto
An yi jana'izar Hakimin Ƙauyen Kulodo, babban ɗansa da wasu mutum huɗu a ranar Asabar cikin alhini, bayan da ƴan bindiga s**a kashe mutane shida tare da yin garkuwa da mutum huɗu a harin da s**a kai ƙauyukan Kulodo da Kwamtsi da yammacin ranar Alhamis a Ƙaramar Hukumar Bodinga ta Jihar Sokoto.
Mazauna yankin sun bayyana cewa kimanin ƴan bindiga 150 ne ɗauke da babura s**a mamaye ƙauyukan, inda s**a riƙa harbe-harbe ba tare da bambanci ba, sannan s**a bi gida-gida suna kwashe kuɗi, wayoyin hannu da kuma fiye da dabbobi 200.
Rahotanni sun ce an harbe Hakimin da babban ɗansa a ƙofar gidansu yayin da suke ƙoƙarin tserewa. Wadanda s**a tsira sun shaida wa jami'an agajin gaggawa na Red Cross cewa yawancin waɗanda aka kashe an harbe su ne a cikin gidajensu.
Wani mazaunin yankin, Alhaji Shehu, ya ce ya yi asarar sama da naira miliyan ɗaya tare da shanu 40 da aka kwashe masa.
An samu damar kwaso gawarwakin ne da yammacin ranar Juma'a bayan jami'an tsaro da manyan jami'an gwamnatin jihar sun isa yankin, saboda fargabar cewa ƴan bindigar na iya kasancewa a kusa.
Sakataren Gwamnatin Jihar Sokoto, Muhammad Bello Sifawa, ɗan majalisar tarayya Nasiru Bobo, da Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Sokoto sun halarci jana'izar, wadda aka gudanar bisa koyarwar addinin Musulunci.
Harin, wanda ya yi sanadin mutuwar mutum shida, raunata biyu da kuma sace mutum huɗu, ya sake tayar da damuwa kan matsalar tsaro a yankunan karkara, musamman yadda ƴan bindiga ke kai hare-hare har kan sarakunan gargajiya a gidajensu.
04/07/2026
Ana zargin wani da safarar yara, Sunday Onome, da amsa cewa ya sayar da ɗan abokinsa kan kuɗi Naira miliyan 1.3, lamarin da ya tona asirin wata sabuwar hanyar safarar yara da ‘yan sanda s**a ce tana gudana tsakanin jihohi.
04/07/2026
Tanimola kalma ce ta Yarbanci wadda ke nufin “Wa ya san gobe?” Kuma da yake babu wanda ya san abin da gobe za ta zo da shi, watakila Dolapo Babatunde Tanimola bai san cewa ba zai kasance a raye ba lokacin da zarge-zargen da ake masa s**a bazu a intanet ba.
Har zuwa wannan makon, sunan Dolapo Babatunde Tanimola bai shahara ba a wajen ƙananan abokan hulɗarsa. Sai dai bayan fadar shugaban ƙasa ta bayyana marigayi Tanimola a matsayin mutumin da ake zargin Prince Adeniyi Adeyemi ya shaida wa masu bincike cewa shi ne ya taimaka masa wajen samun takardar naɗin mukamin Darakta Janar na wata ƙungiya ta bogi mai suna Presidential Foreign Intervention Promotion Council (PFIPC) da yanzu take ƙarƙashin bincike, hankali ya koma kan mutumin.
Mutuwarsa ta bar wani muhimmin ɓangare na binciken a duhu, domin yanzu masu bincike ba za su iya samun bayanai kai tsaye daga gare shi ba.
04/07/2026
MURIC za ta kai ƙara Kotun Koli kan hana sanya hijabi a makarantar Oyo
Ƙungiyar MURIC ta bayyana cewa za ta kai ƙara zuwa Kotun Koli domin kalubalantar hukuncin da ya tabbatar da hana ɗalibai mata sanya hijabi a makarantar International School ta Jami’ar University of Ibadan.
Click here to claim your Sponsored Listing.
Website
Address
Zaria