MATSIRGA ISLAMIC RESOURCES

MATSIRGA ISLAMIC RESOURCES

Share

20/06/2023

NUHU RIBADU YA DACE

Daga Malam Bello Muhammad Sharada

Matsalar tsaro a Najeriya tana bukatar mai amana, kuma tana bukatar zakakuri. Ana kashe makudan kudaden jama'a a wajen harkar tsaro. Tsaro ya fi komai cin kudaden Najeriya, ya wuce abin da ake kashewa a 'Petrol subsidy.' Samar da tsaro kuma babban wajibin hukuma ne, shi ne abu daya cikin biyu wanda yafi damun kasarmu. MAFI girman dalilin da ya sa aka kasa shawo kan matsalar tsaro akwai rashin jagoranci mai amana.

Baiwa Ruhu Ribadu mukamin National Security Adviser NSA an ajiye kwarya a gurbinta. Kamar saka Janar Buba Marwa ne a NDLEA. Da Nuhu Ribadu da Buba Marwa duk Fulanin jihar Adamawa ne, dukkansu Yan siyasa ne da s**a taba tsayawa takarar shugabancin Najeriya, kuma s**a rike manyan hukumomi EFCC da NDLEA.

Ina zato a karkashin Ribadu za a iya samun canji na alheri a harkar tsaro ta Najeriya.

18/06/2023

ZAI YI KYAU GWAMNA ABBA DA MADUGU SU SAKE NAZARI

Daga Malam Bello Muhammad Sharada

A dan tsahirta na kwana biyu a duba sosai a ga guraren da aka yi kuskure a gyara. A sake dubawa a ga ina aka yi ganganci a dau mataki don a guji gaba. A kalla da idon basira ina ne ya kamata a tabbatar an dauki mataki a yi hakan.

Kada a ji nauyin yin abin da ya dace. Haka Kada a ji kunya ko tsoron masu wargi. Amma kuma shugabanni su sani sun yi rantsuwa da daukar alkawarin zasu yi aiki da adalci da amana. Babu I'll will. Babu sani ko Sabo.

Abin da ya sa na fadi haka, mutanen da ake mulka suna kuka. Ya kamata a saurari kokensu. Sannan kuma jama'a sune gwamnati, aikin farko na gwamnati shi ne samun walwala da tsaron lafiya da rai da dukiyar jama'a. A kula da wannan.

Wata jarida, mallakin kamfanin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ta ce a cikin sati biyu Gwamna Abba K Yusuf ya rusa dukiya ta kusan naira biliyan 126. A duba lamarin nan, a kalli salon da ake amfani da shi.

KAI KUMA SSG Dr Baffa Bichi, yanzu mulki kuke yi, ba kamfen ba. An gama siyasa, a maida hankali a cikawa mutane alkawuran da aka dauka. A yi musu abin da ya dace da kudinsu kuma a rike amana. Banda hargagi da zumudi da wauta. KO ina ake son zuwa za a je

Photos from MATSIRGA ISLAMIC RESOURCES's post 17/06/2023

DA KYAW ABBA GIDA GIDA DA TALLAFIN KARATU

Yau Abban Kanawa ya wayi gari da bude damar karo karatu ga mabukata na lungu da sakon jihar Kano Musamman masu first class

Kuma maganar gaskiya wannan na daga dalilai da s**a sanya galibin Kanawa musamman matasa yin tsayuwar daka na zaben Abba dayi masa aikin dan ganin yayi nasara

Kuma shima wannan na daga cikin alkawurran daya dauka a lokacin yakin neman zabensa a 2019 da kuma 2023
Allaah yayi masa jagoranci kan hakan da sauran manufofinsa na Alheri

Amma ni a irin nawa tsokaci da karamin sanin a fannin ilimi (Education) da muke yan farawa

Da farko tsakanin mai fara Digirin farko da mai cigaba dana biyu wanne yafi bukatar tallafi ?

Na biyu mai first class da wanda ya Gama da pass Digiri wanne yafi bukatar tallafi?

Na uku masu fara Digirin farko dana biyu zuwa uku wanne s**afi yawan da in an rage an samu cigaba?

Dalilina kuwa shekarun baya munyi wata Daura (seminar) bayan an kammala masu rabo s**a samu mu da bamu da rabo muka rasa dan mutum goma 10 kacal za'a dauka

sai hukumar shirya jarrabawar s**ayi la'akari da Dalubai mabukata wannan karatu amfi mutum dari 100 wurin jarrabawar sai s**ayi duk mai yiwuwa aka dauki mutum 50

Na biyu shekaru 4 da s**a wuce mun sake wata Daurar ta larabci za'a dauki mutum 20 masu Digirin farko
Mutum 20 masu Digiri na biyu a Abuja zuwa Turkiyya

Bayan an kammala sai s**ayi la'akari da Dalubai masu son Digirin farko sunfi yawa sai s**a sake daukan 20 cikin wanda makinsu ya kai cikin masu Digirin farko a wannan 20 na biyu da aka kara nima sunana Usman Matsirga ya fito Alhamdulillah ban samu tafiya ba sabida wasu dalilai masu karfi
kaga kenan sun dauki 40 a Digirin farko 20 a Masu Digiri na biyu

Tambayan da galibin Dalubai masu Digiri na biyu s**ayiwa FARFESA Hamaduddeen kenan yaya su ba'a kara dauka cikin su ba?

Amsar kenan da yayita baiwa kowa mai son Digirin farko yafi mai son Digiri na biyu bukatar karatu da kuma Tallafi.

Da wannan nake ganin mai Tatata yafi bukatar tallafi sama da wanda ya iya tafiya harda guje guje

Ina fatan yan uwa zasu fahimce ni

In kuma akwai wani Karin Haske a fannin ilimi da ban sanshi ba?
Ko ta Bangaren gwamnatin Kano a taimaka mana dashi dan mu karu kuma mu karar
Dan mun san Gwamnati nada FARFESOSHI DAKTOCI da GOGAGGUN Ma'aikata a Fannin Gudanarwar ilimi ( EDUCATION )

Allaah Muke roko ya dafawa gwamnatin Abba bisa kudurinta na ilimi da ilmantarwa dama kowace gwamnati
Allaah ka dafawa gwamnatocinmu kan alheransu ka kare mu daga sharrori da munanan manufofin da baza su amfani Al'ummah ba.

[email protected]
27/11/1444 Hijrah 16/06/2023 Miladi.

Want your business to be the top-listed Shop in Utako?
Click here to claim your Sponsored Listing.

Category

Telephone

Website

Address

Opp Liman Street Along Madalla Die Die Dakwa Niger/Abuja
Utako