Sani Shuaibu Suleman

Sani Shuaibu Suleman

Share

27/06/2023

ADDU'A IDAN MAI AZUMI ZAI BUDA BAKI

ذهب الظمأ، وابتلت العروق، وثبت الأجر إن شاء الله.

Ma'ana: Kishirwa ta tafi, an yayyafawa jijiyoyi ruwa, kuma lada ya tabbata in Allah Ya So.

Abdullahi bn Amr bn al-As ya ce Manzo Allah, Tsira da amincin Allah Su tabbata a gare Shi, ya ce: "Mai Azumi yana da addu'a da Ba a mayar da ita Idan ya Zo Bude baki”. Abdullahi bn Amr ya Kasance Idan ya zo Bude Baki Sai ya ce;

اللهم إني أسأللك برحمتك التي و سعت كل شي ء إن تغفر لي

Ma'ana: Ya Allah! Ina Rokon ka Saboda Rahamarka da ta yalwaci komai, ka gafarta mini.

© Sani Shuaibu Suleman

01/12/2022

HANA GABA DA KAURACEWA JUNA

Daga Abu Huraira RA ya ce: Manzon Allah SAW ya ce: ana bude kofofin Aljannah duk ranar litinin da ranar alhamis, sai a yafe wa duk bawan da ba ya yin shirka da Allah , amma banda mutumin da yake gaba da dan uwansa, sai a ce: Ku kyale wadannan har sai sun yi Sulhu; Ku kyale wadannan har sai sun yi Sulhu; Ku kyale wadannan har sai sun yi Sulhu.

Muslim ne ya ruwaito.

01/12/2022

KWADAITARWA KAN YIN SANA'A

Daga Abu Huraira ya ce: Na Ji Manzon Allah yana cewa: dayanku ya fita da safe ya yi itace ya dauko shi a gadan bayansa (da niyyar yin Sana'a) ya yi sadaka da shi ya wadatu daga rokon mutane, ya fi alheri a gare shi kan ya roki wani, shi kuma ko ya ba shi , ko ya hana shi. wannan kuwa saboda hannun da yake sama ( mai kyauta) ya fi hannun da yake kasa (mai kar6a). kuma ka fara (wajen ciyarwa) da iyalinka.

Bukhari da Muslim s**a ruwaito shi.

Want your public figure to be the top-listed Public Figure in Kano?
Click here to claim your Sponsored Listing.

Category

Website

Address

Kano