Zulfiqa Redio

Zulfiqa Redio

Share

Photos from Zulfiqa Redio's post 18/01/2026

Kisan uwa da 'yayanta a Kano: 'Yansanda sun k**a dan 'yar uwar marigayiyar da wasu mutane 2 da ake zargi da kisan

Rundunar ’Yansanda ta jihar Kano ta k**a mutane uku da ake zargi da hannu a kisan gillar wata uwa da ’ya’yanta shida da aka yi a unguwar Dorayi Chiranchi da ke cikin birnin Kano.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ƴansandan jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar a ranar Lahadi.

Kamen ya biyo bayan wani aiki na musamman bisa bayanan sirri, wanda aka gudanar bisa umarnin sufeto janar na ’Yansanda, Kayode Egbetokun, tare da kulawar kwamishinan ’Yansanda na jihar, Ibrahim Adamu Bakori.

A cewar rundunar, an k**a wadanda ake zargin ne a wani samame da aka gudanar daga karfe 10:00 na dare a ranar 17 ga Janairu zuwa karfe 4:00 na asubahin ranar 18 ga Janairu, 2026.

Wadanda aka k**a sun hada da Umar Auwalu, mai shekaru 23 daga unguwar Sabuwar Gandu; Isyaku Yakubu da aka fi sani da “Chebe”, mai shekaru 40 daga unguwar Sagagi; da Yakubu Abdulaziz wanda aka fi kira “Wawo”, mai shekaru 21 daga unguwar Sabon Gida Sharada.

’Yansanda sun bayyana cewa wanda ake zargin jagorantar kisan, Umar Auwalu, wanda dan uwa ne ga marigayiyar, ya amsa laifin aikata kisan. Haka k*ma, ya bayyana cewa sun aikata wasu kashe- kashe masu tada hankali a wasu sassan Kano a baya-bayan nan.

Daga cikin abubuwan da aka kwato daga hannun wadanda ake zargin akwai tufafi masu tabon jini, wayoyin salula biyu na marigayiyar, adda, gora, kudi da ake zargin an kwace a wajen da abin ya faru, da wasu mak**ai masu hadari. Rundunar ta ce bincike na ci gaba.

Rundunar ’Yansanda ta Jihar Kano ta yaba wa jami’an da s**a gudanar da aikin, tare da gode wa al’umma bisa addu’o’i, goyon baya da hadin kai. Rundunar ta k*ma tabbatar wa jama’a kudirinta na ganin an gurfanar da duk masu aikata laifuka a gaban kuliya.

Photos from Zulfiqa Redio's post 01/09/2025

RUNDUNAR YAN SANDAN JAHAR KATSINA TA CAF-KE MASU SADARAR MAKAMAI A JAHAR KATSINA.

— Real ßàqír Yúsûf Adam

An Cafke Mutane 2 Dauke da Bindiga da Harsasai Sama da 1,200 a Jihar Katsina

A ranar Litinin, 1 ga watan Satumba, 2025, jami’an tsaro sun samu nasarar cafke wasu mutane biyu da ake zargi da laifin mallakar bindiga ba bisa ƙa’ida ba, a yankin Ingawa, jihar Katsina.

Wadanda aka k**a sun hada da *Abdulsalam Muhammad*, mai shekaru 28, da *Aminu Mamman*, mai shekaru 23, dukkansu ‘yan asalin *garin Baure*, karamar huk*mar *Safana*, jihar Katsina.

Rahotanni sun nuna cewa an k**a mutanen ne dauke da *bindiga kirar mashin gun* da *harsasai 1,295*, a cikin wata *mota kirar Golf, mai launin shudi, lamba RSH 528 BV*.

Wannan samame ya faru ne a kan hanyar garin *Karkarku* da ke karamar huk*mar *Ingawa*, yayin da wadanda ake zargin ke kan hanyarsu daga *Hadejia*, jihar Jigawa zuwa *Katsina*.

Jami’an tsaro sun bayyana cewa bincike ya na cigaba, k*ma za a gurfanar da su a gaban kuliya bayan kammala cikakken bincike.

A ƙarshe, huk*momi sun nemi goyon bayan jama’a da addu’o’i domin tabbatar da zaman lafiya da dakile aikata laifuka a yankin.

---

— Zulfiqar Redio Nigeria

Want your public figure to be the top-listed Public Figure in Kano?
Click here to claim your Sponsored Listing.

Category

Telephone

Address

Kano Kofar Waika
Kano
NAIBAWA