Taskira Hausa

Taskira Hausa

Share

31/07/2023

SHUGABA TINUBU YA JI KOKEN KU

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya fito gaba haɗi domin share kukan al'ummar ƙasa musamman dangane da halin matsi da ake ciki.

A jawabin da ya gabatar ta kafafen yaɗa labarai a yammacin yau ya bayyana yadda gwamnati ta shirya antayo maƙudan kuɗaɗe ta fannoni da dama domin ragewa mutane raɗaɗin gyaran karayar tallafin mai da ake ciki a halin yanzu. Ga kaɗan daga cikin tanade-tanaden:
1. Bawa masu masana'antu 75 jari mai rangwame har na naira biliyan ɗaya kowannen su. Wanda za su biya a tsahon watanni 60.

2. Masu matsaƙaita da ƙananan sana'o'i za su amfana da naira biliyan 125 domin haɓɓaka jarinsu.

3. Daga cikin waccan biliyan 125 gwamnati za ta bada jari kyauta (mai haɗe da sharaɗi) na naira 50,000 ga masu ƙananan sana'o'i mutum 1,300 a kowace ƙaramar hukuma.

4. Sauran biliyan 75 za su tafi wajen masu matsaƙaitan sana'o'i inda za a bawa mutum 100,000 rance mai rangwame na naira 500,000 zuwa miliyan ɗaya wanda za su biya a hankali cikin shakara uku.

5. Tunda sai da ruwan ciki ake janyo na rijiya, Shugaban Ƙasa ya bada umarnin fito da abinci har ton 200,000 tare da takin zamani ton 225,000 domin rabawa ga mabuƙata da manoma.

5. Nan ba da jimawa ba gwamnati za ta samar da ƙananan moticin bus masu amfani da gas har guda 3,000 domin kawo rangwame a kuɗin sufuri da jama'a ke fama da shi. Waɗannan motoci za a raba su ne ga kamfanonin sufuri domin gudanar da su.

6. Haka nan kuma gwamnati ta ware maƙudan kuɗaɗe domin noma hekta 500,000 a ɓanagarori daban-daban na ƙasar nan. Baya ga samar da abinci wannan shiri zai samarwa da matasa marasa aikin yi sana'a ta wucin-gadi.

A ƙarshe, ga waɗanda s**a saurari cikakaken jawabin za su ji yadda Shugaba Tinubu ya nuna tausayawa da halin da ake ciki, ya bada haƙuri, ya kuma sha alwashin ƙawo ƙarshen wannan yanayi cikin gaggawa da taimakon Allah.

©Abdulaziz Abdulaziz

08/07/2023

TARBIYYA DA AL'ADAN JAGORORIN AL'UMMA A KASAR HAUSA

A shekarun da s**a shud'e da yawan masu rike da sarautun gargajiya k**a daga Mai Unguwa, Dakace, Malamai, Shuwagabannin Matasa, Hakimai, har zuwa Sarki da sauran su, sune keda hakkin kula da tarbiyan jama'an su bayan iyaye a cikin gida.

Shiyasa ma a wancan Lokacin zaka ga Sarki shine Limamin Gari, Alkali, Jami'in tsaro da Sauran su.

Duk matashi ko yaro A cikin Unguwa daya daga cikin Jagororin da na lissafa suna Iya hukunci akan matasa da yara a cikin Unguwa ko dan Waye saboda gyaran tarbiya, da fadin "bahaushe da yace gyara kayan ka bazai zamto sauke mu raba ba".

A duk Lokacin da akace matasa zasuyi abinda s**a so a unguwa Kuma Babu Mai tsawata masu to gaskiya sai abinda s**ayi, saboda kafin ace aje gurin hukuma abu ya lalace.

Yanzu a misali sai ace a cikin Unguwa kuga Wani Yana bata maku yaro da neman sa ta baya, sai ku ki hukunci a kansa Saboda daukan doka a hannu babu kyau? Ko yaro acikin gidan ku yana rashin tarbiya sai a zura masa ido ko a tsaya jiran hukuma har tazo ta gyara tarbiyan sa?

Misalin irin abinda yafaru kenan a Zaria da dakataccen basarake Marafan Yamman Zazzau da Wani matashi wanda yake zargi yana bata wani a cikin wani kango, Wanda a matsayin sa na Mai saurauta a Masarautar Zazzau Kuma wakilin al'ummar Unguwan Magajiya dake Zaria yayi amfani da damar sa na jagora ya hukunta sa daidai gwargwado saboda hakki na makota ka da hakkin tarbiyan matasan yankinsa a Wanda yarataya a hannun su.

Bayan hukunci da dakataccen Basarake Marafan Yamman Zazzau yayi akan matashin da ake zargi da lalata yaran mutane a unguwa Hakan yasa wasu maras kishin al'umma sun shiga media sunata bata masa suna, Wanda mu a yankin mu ta kasar hausa musamman a Yanzu munada bukatan irin wadannan mutane. Saboda duk Wanda yake bin wasu ta baya Shima ana binsa Kuma Suma yaran da yabi zasu bi wani kaga daga nan duk Al'umma zata gurbace da tarbiya irin ta zamanin al'umman Annabi Lud'

Kuma harda wasu manya sune da shiga gidan Radio suna bata Alh. Mustapha Adamu Ubaidu dakataccen (Marafan Yamman Zazzau) akan wannan lamari, Kuma mu Muna ma da tambaya wai shin meye ke tsakanin wadannan mutanen da suke fita Radio da wannan matashi da ake zargi da bin Maza? Sannan Suma sauran masu ruwa da tsaki da s**a ruwa s**ayi Tsaki, meye nasu aciki.?

Sannan har ila yau shifa Mai Girma dakataccen Marafan Yamman Zazzau dinnan shine Jagoran 'yan sintiri na tsaron yankin su, Wanda kullun basa bacci Domin bada kariya ta tsaro ga yankin Unguwan su ta Magajiya a irin kokarin nasa yasa aka dauki 'yan sintiri da duk wata shi ke biyan su albashi, so a wannan yanayin ne fa yaga Wani na aikata ba daidai ba yayi hukun ci a Iya matsayin sa na Jagoran al'umma a unguwa sai wasu s**a fake da haka saboda Wani abu daban dayake a ransu na hassada.

Mufa mutanen Zaria wayayyu ne, bamu kin namu don ayabemu kuma waya tabamin dana in tabi nasa baya cikin al'adun mu.

Muna kira na gagggawa Domin yima masarautar Zazzau da basaraken ta adalci.

Ahmed Tijjani
Media Consultant,
Marubuci, Danjarida, Mai kishin Masarautar Zazzau.

Photos from Taskira Hausa's post 28/07/2022

YADDA RIMAYEN ZAZZAU S**A SAMO ASALIN SUNAYENSU A
TARIHI

Zariya tana da wasu rimaye masu tarihi a cikin ganuwar garin. Idan aka ce zariya, ana nufin dukkan garin ciki da waje abin da ya shafi Sabon Gari, da Samaru da Basawa da Wusasa da Tudun wada, duk da gefen wadannan wurare duk zariya ake cewa. To, amma ainihin cikin garin zariya, shi ne inda ganuwar zariya ta zagaye garin, shi ne a Turance, Turawa suke kira “ZARIA CITY” Watau cikin garin zariya inda kofofin nan guda takwas suke hade da ita, watau Kofar Bai, Kofar Doka, Kofar Kibo, Kofar Jatau, Kofar Kuyan Bana, Kofar Gayan, Kofar Kona da Kofar Galadima.

A cikin wannan gari na zariya akwai wasu rimaye guda shida (6) wadanda ake masu lakabi da irin abin da ke tare da su ko ta sanadin sunan mutum ko Dabba ko kuma dalilin wani abu da ke faruwa a wurin, wadannn Rimaye su ne, Rimin Tsiwa da Rimin Kwakwa, da Rimin Doko da Rimin Kambari da Rimin Danza da Rimin Bindiga.

Tasawirar rimiRimi-
RIMIN TSIWA: Yana kan t**in da za ka shiga cikin Unguwan Rimin Tsiwa a gefen T**i a kofar gidan Sarkin zazzau Muhammadu Aminu. Kuma ta can tsallake akwai tsohon gidan Ajiyan zazzau Alh. Sani Rimin Tsiwa. Ana kiran wannan rimi da wannan Suna a dalilin wasu tsuntsayen s**an ta kuka “TSIW TSIW”. A sak**akon wannan kukan ya sa aka sa ma wannan Rimin Tsiwa fiye da shekaru dari biyu da s**a gabata. Kuma har yanzu sunan Unguwar kenan. Kuma a nan ne zuri’ar Malam Abdulkarimu, Sarkin zazzau , s**a zauna, watau gidan sarautar Katsinawan Zazzau. Amma yanzu wannan Rimin ba ya nan an sare shi a lokacin Mulkin Janar Ibrahim Badamasi Babangida, tsohon shugaban Kasar Nijeriya, saboda gyaran hanyar zariya.

RIMIN KWAKWA: Wannan Rimi na makwaftaka da Rimin Tsiwa kuma an sami wannan suna na Rimin Kwakwa a dalilin wasu tsuntsaye ne da Allah ya zaunar da su a wajen ko kuma kan Rimin. Su wadannan tsuntsaye suna da k**a da Zalbe ko Shamuwa, amma ba shamuwa ba ce kuma ba zalbe ba ne. Kuma su ma suna da dogon baki da tsawon kafa.zariya.

A dalilin zamansu a wannan Rimi ya sa ake kiran Rimin ko wurin da Rimin kwakwa. Wannan Kwakwa na bayyana irin kukan da suke yi. Suna yin kuka k**ar haka ” KWA, KWA, KWA.” Wannan shi ne dalilin kiran wannan wuri da sunan Rimin kwakwa kuma har yan zu ana kiran wurin haka.zariya.

Wannan Rimi yana a tsakanin hanyar zuwa gidan Sa’in Zazzau Umaru Jume. Yanzu wannan Rimi an sare shi lokaci guda da Rimin Tsiwa a lokacin Mulkin Janar Badamasi Babangida lokacin da ake gyaran hanyar cikin garin zariya.zariya.

RIMIN DOKO: Rimin Doko , yana Unguwar Kaura ne kuma ya sami wannan suna ne a dalilin wanban Zazzau Malam Marwa Doko, dan Sarkin zazzau Yamusa na gidan Sarautar Barebari na zazzau. Wannan Rimin yana kofar gidan Sarkin zazzau Malam Yamusa ne amma ana kiran gidan da GIDAN DOKO. Kuma nan ne Cibiyar gidan Sarautar Barebari na Zazzau. A Rimin Doko Wambai Doko yake zama a da. Kuma dalilin haka ne ya sa ake ce ma wurin Rimin Doko.

RIMIN KAMBARI: wannan Rimin yana kan t**in Unguwar Kaura da hanyar da ta nufi Unguwar Nufawa ta t**in kaura din., Rimin Kambari ya sami wannan suna ne a dalilin mutanen kambari da s**a zauna zariya suna cinikayya da mutanen gari. Su Kambarawa mutanen wajen Yobe da Fika ne. A wannan gindin Rimi suke zama da shugabansu da ake kira Kambari, a dalilin haka ne wurin ya sami suna da kuma Rimin.

RIMIN BINDIGA: Rimin Bindiga shi ma makocin Rimin Kambari ne, Kuma shi yana da dadadden tarihi tun lokacin Mulkin Habe. Tanan Sarki ke bi idan zai fita gari ta Kofar Kuyambana ko Kofar Gayan daga Fadar Bono. Saboda haka idan ya fito nan za a dinga buga bindiga don a san Sarki ya fito yana tafe. Wani kaulin kuma ance, a nan ne wani Sarkin bindiga ya zauna tun a lokacin zuwan daular Mulkin Fulani a Zazzau. To, koma yaya ne dai, yanzu Rimin yana nan a kusa da gidan Wanban zazzau Usman dan Galadima Zubairu dan Sarkin zazzau Malam Yero na gidan Sarautar Barebari.

RIMIN DANZA: Rimin Danza shi ma yana da dadadden tarihi, da ke da alaka da wani maharbi mai suna Danza kuma a dalilin sunansa ake kiran wurin Rimin Danza. Wannan Rimi masana tarihi sun ce ya sami sunansa ne dag wani gari da ake kira Danza cikin kasar Giwa, a hanyar Karaukarau zuwa Kadage. An ce sunan wani maharbi ne, da ya tashi daga garin ya dawo zariya. Akwai Rimi a kofar gidansa sai aka wayi gari Aljanu sun tunbuke Rimin sun biyo shi da shi zuwa Zariya.

Wani kaulin kuma an ce sunan wani Sarki ne daga cikin sunayen Sarakunan Habe na Zazzau. Ana kiransa da Danzaki kuma shi ya kafa garin da ya tashi daga garin ya shigo zariya shi ne ya zauna a nan dalilin da ya sa ake ce wa wannan Rimi, Rimin Danza. To kodai yaya ne wannan Rimi yana nan a wani wuri. In ka fita ta hanyar zuwa kofar Kuyambana ta Durumin mai Garke zuwa Town School No. 1 sai ka bi ta jikin makaranta har zuwa Rimin Danza kusa da gidan wani sanannen Attajiri marigayi Alhaji Dahiru Kanti.

Wannan shi ne takaitaccen bayani a kan tarihin wadannan Rimaye na zariya, kuma ko da ma zariya an san ta da Rimaye don har ana mata kirari da cewa ” RIMAYEN ZARIYA SUN FI ‘YAN MATAN ZARIYA ALKAWARI” kuma ana cewa ” RIMI ADON GARI A BIRNIN ZARIYA”

Sauran Rimaye da suke wurare, yawancin su duk an shuka su ne ko a gona ko kan t**i har ma a gida. Kamar yadda wani kauli na tarihi yace ” Rimayen da s**a tashi daga Babban Dodo cikin garin zariya s**a jeru har zuwa Tudun wadan zariya an shuka su ne a zamanin Sarkin zazzau Malam Aliyu Dan Sidi n gidan sarautar Mallawa, bisa umurni da shawarar Turawa a lokacin Mulkin Turawan Ingilishi. Haka kuma mutane kan zo daga wasu kasashe ru rayi irin wannan Rimi su je su shuka a kasarsu, sannan ana zuwa a sayi itacen wanda ya girma sare a sassaka Jirgin KwaleKwale don masu fito a ruwa.

Kuma har ila yau ana amfani da ‘ya’yan wannan rimi inda ake cire audugar ciki a don yin Katifa da Matashi da Kahu da Hunhu na Hawa doki don yanzu Haka akwai Anguwan da suke wannan sana'a a Birnin Zazzau wato unguwa Kahu sannan suna da Shugaban wannan Sana'a wato Wakilin Kahu
Allah ya daukaka musulunci da musulmai ya Kara daukaka Garin Zazzau

Want your business to be the top-listed Media Company in Gwarinpa?
Click here to claim your Sponsored Listing.

Telephone

Website

Address

Police Station Road
Gwarinpa