Al Amsal
01/03/2026
Wannan ita ce Amurka, ana tsaka da tattaunawa, sun kàshe Jagoran addinin ƙasar Iran Ayatollah Khamenei. Kar ku manta sun sacé Nicolas Maduro, shugaban kasar Venezuela fa.
Yanzu, don Allah, ku da ake tattaunawa da ku kan matsala, ku ne kuma kuke ta’àddànci. Allah Ya yi gaskiya, wallahi.
“Suna faɗi da bakunansu abin da ba ya cikin zukatansu.” Suratu Ali-Imran 3:167.
Mu ’yan Nigeria, musamman ’yan Arewa, babu abin da wannan zai tuna mana sai mu dage da addu’a. Wallahi babu wani abu da zai dakatar da Amurka a wannan duniyar sai Allah. Kuna ganin Iran da Venezuela kawayen Russia da China ne, amma me s**a tsinana musu?
Maganar cewa ana kàshe Kiristoci a Nigeria, kuma Amurka ta dage a kai, tabbas akwai manufa a ƙarƙashinta, sunce ana take hakkin Dan adam a Iran da Venezuela ma, a jiya kawai yara kanana yan makaranta sama da 80 s**a kàshe a Iran.
Addu’a ce kawai za ta kare mu daga sharrinsu. Ya Allah ka kare mu daga sharrin zalunci.
01/03/2026
LABARAI | ABIN MAMAKI DAGA HABASHA
Wani dattijo mai suna Isaac Adamo, dan shekaru 78, ya bayyana tarihin rayuwarsa da ya dauki hankalin jama’a, inda ya auri mata 23 tare da haifar da ’ya’ya 70.
Isaac Adamo na zaune ne a garin Malabi, yankin Oromia a ƙasar Habasha (Ethiopia). Ya auri matarsa ta farko ne yana da shekara 23, kuma cikin tsawon shekaru 55 da s**a biyo baya, ya kara aure har ya kai mata 23.
A cewarsa, bai wuce shekara guda ba tun da ya auri amaryarsa ta ƙarshe, wadda ita ce ta 23 a jerin matansa. A halin yanzu, ƙaramin ɗansa ko ’yarsa na da watanni uku, yayin da babban ɗansa ya kai shekaru 53.
Isaac Adamo ya shahara wajen kiwon dabbobi, inda a wani lokaci ya mallaki dabbobi sama da 800. Ya bayyana cewa yalwar dukiya ce ta sa yake yawan aure.
> “Nakan yi aure duk lokacin da nake so, saboda ina da shanu da yawa, ina da dukiya da kadarori,” in ji shi.
“Dogarona a rayuwa shi ne kiwon dabbobi; ina da raƙuma, shanu da awaki masu yawa.”
Ya kuma ce yana yin aure ne a duk lokacin da ya rabu da ɗaya daga cikin matansa.
> “Idan na ga mace mai kyau, sai na saki ɗaya daga cikin waɗanda nake tare da su, na auro wata,” in ji Isaac.
Matarsa ta farko ta rasu, yayin da a yanzu yake tare da mata uku kacal, bayan ya rabu da mata 19. Ya ce wasu rabuwar ta faru ne sakamakon saɓani, wasu kuma ba tare da wani dalili na musamman ba.
Daga cikin ’ya’yansa 70, akwai maza 36 da mata 34. Isaac ya bayyana cewa a yanzu ba shi da niyyar ƙara aure.
A cewarsa, idan aka haɗa ’ya’yansa da jikokinsa, iyalinsa sun kai mutum 279. Sai dai ya amince cewa dukiyarsa ta ragu a yanzu idan aka kwatanta da baya.
Babban ɗansa na da suna Ibrahim, yayin da ƙarama kuma ake kiranta Dahab. Isaac ya ce mutane da dama kan tambaye shi yadda yake kula da tarbiyyar wannan adadi na ’ya’ya, amma a ganinsa hakan bai da wahala matuƙa, musamman idan akwai dukiya.
Yanzu haka, labarin rayuwar Isaac Adamo na ci gaba da janyo muhawara da mamaki a tsakanin jama’a.
18/02/2026
DA DUMI-DUMI | Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir el-Rufa'i, ya gaza cika sharaɗin beli da humumar yaƙi da masu yiwa tattalin arziƙin ƙasa tu'annati EFCC ta ba shi a yau.
Sharaɗin belin dai shine; sai el-Rufa'i ya kawo wani Sakataren din-din-din (Permanent Secretary) da kuma wani darakta Janar a ma'aikatar gwamnatin tarayya.
Majiyar mu ta tabbatar ma na cewa; wani Sakataren din-din-din a ma'aikatar gwamnatin tarayya da ya fara zuwa ofishin hukumar EFCC domin tsayawa el-Rufa'i ya ji tsoron tsaya ma sa, inda ya janye daga tsayawa el-Rufai a hukumar ta EFCC.
Yanzu haka dai el-Rufai zai cigaba da zama tsare a hukumar ta EFCC — a daidai lokacin da itama hukumar nan ta ICPC ta aiko masa da takardar gayyata domin ta bincike shi.
30/01/2026
Munafurci ne wannan!
Majalisa ta ba da umarni a yi amfani da jiragen yaki da sojojin kasa don kai manyan hare-hare a wasu sassan jihar Gombe - Duba yankunan da za a farmaka a sashen sharhi.
Hoto: , (X)
Click here to claim your Sponsored Listing.