Giade Daily Post
01/04/2026
Isra’ila: Netanyahu ya ce manufar yaƙin ita ce ɗaga Isra’ila zuwa ƙasar mai ƙarfin tasiri a duniya
Firayim Minista Benjamin Netanyahu ya bayyana cewa rikicin da ake yi da Iran wani ɓangare ne na ƙoƙarin faɗaɗa ƙarfin Isra’ila domin ta zama ƙasa mai tasiri a yankin da ma duniya baki ɗaya.
Ya jaddada cewa ayyukan da ake ci gaba da yi suna daidaita da wata doguwar manufa ta ƙarfafa matsayin Isra’ila a idon duniya.
Ana sa ran wannan furuci zai ƙara tayar da muhawara kan ainihin manufofin yaƙin da kuma yiwuwar sakamakonsa na dogon lokaci.
01/04/2026
Shugaban APC tare da Gwamna Abba Kabir Yusf Sun Gana da Gwamna Bala Mohammed a yau
Shugaban jam’iyyar All Progressives Congress (APC) na kasa, Nentawe Yilwatda, tare da gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, sun kai ziyara ga gwamnan Jihar Bauchi, Bala Abdulkadir Mohammed, a fadar gwamnati da ke Bauchi.
Rahotanni sun bayyana cewa an dauki ziyarar a matsayin ta kashin kai, domin ba a fitar da wata sanarwa ga manema labarai ba, haka kuma ba a yi wata hira da manema labarai ba bayan kammala ganawar.
Click here to claim your Sponsored Listing.
Category
Culinary Team
Attire
Contact the business
Telephone
Address
Bauchi
2023